Jirgin Air India Mai Dauke da Fasinjoji 242 Ya Yi Hatsari a Ahmedabad
Wani jirgin sama mallakin kamfanin Air India wanda ya nufi birnin London ya yi hatsari a birnin Ahmedabad na kasar India, jim kadan bayan tashinsa daga filin jirgin saman birnin.
A cewar wani rahoto da aka samu, jirgin yana dauke da fasinjoji 242 a lokacin da lamarin ya faru. Har yanzu hukumomi ba su fitar da cikakken bayani kan musabbabin hatsarin ba, kuma ba a tabbatar da adadin wadanda suka jikkata ko rasa rayukansu ba.
Ana ci gaba da aikin ceto da bincike a wajen da hatsarin ya faru, yayin da hukumomin tsaro da na kula da sufurin jiragen sama ke gudanar da bincike don gano musabbabin wannan mummunan al'amari.