Gwamnatin Kano ta farfaɗo da matatar ruwa da ta kwashe shekaru 4 ko ɗigon ruwa ba ta samar ba
Gwamnatin jihar Kano ta ce ta farfaɗo da matatar ruwa ta Guzu-Guzu, wacce ta ke samar da lita miliyan 7.2 ta ruwa a rana ga yankin kananan hukumomin Kabo da Rimin-Gado.
Kwamishinan Muhalli da Ruwa da Canjin Yanayi, Dr. Dahir M Hashim ne ya baiyana hakan a yau a Kano.
Ya ce aikin farfaɗo da matatar ya haɗa da injin jannareto mai ƙarfin 800KVA, gyaran fayif-fayif hudu da kuma gyaran dakin da ke tunkudo ruwan da kuma ofisoshin ma'aikatan wajen
Hashim ya ce nan da gobe mazauna yankin za su fara ganin ruwa a famfunan su a wani mataki na gwaji yayin da ake ci gaba da aikin don farfaɗo da matatar na dindindin.
Ya ce gwamnatin gwamna Abba Kabir Yusuf a shirye ta ke ta farfaɗo da duk karatun ruwa 19 na jihar dan samar da wadataccen ruwan sha ga al'ummar Kano
